TASKAR
AJALI!!!
Littafi
Na Daya (1)
Part
A
BUDUWARCE
'yar kimanin shekaru goma sha tara,ma'abociyar kyawu irin wanda a ganin farko
zata ruda dukkan 'da namiji dayayi arba da ita musamman a cikin irin wannan
shiga
da tayi ta ratso
tsakiyar kasuwa.Riga da wando
ne na fatar damisa matsatstsu ta sanya wadanda
suka baiyana
dukkan
kyakyawar siffar
jikinta,kuma
a bayanta ta
ratayi
wata zabgegiyar takobi.Kallo
daya
zaka yiwa
wannan
budurwa ka tabbar da
cewa
jaruma ce
domin
tana da kira irin ta
sadaukai.Ta
daure dogon
gashin
kanya mai kyalkyali ya zuba
a
bayan
kafadarta
har bisa
mazaunanta.Tsananin
kyawunta
da
kwarjinita ne yasa gaba dayan
jama'ar
dake cikin
kasuwar
suka tsayar da harkokinsu
suka
zuba mata
na
mujiya kai wasu ma yan
kasuwar
basu san
sa'adda
suka rinka tsallake hajarsu
ba
suka rinka
binta
a baya domin ta tafi da
imaninsu.Bawai
maza
ba
hatta mata masu siye da masu
siyarwa
watsar da
komai
sukayi suka rinka bin
wannan
bakuwar
budurwa
a baya don kawai su san
ko
ita wacece da
kuma
abinda ya kawo ta cikin
wannan
kasuwa.Dama
a
guje wannan budurwar ta fado
cikin
kasuwar
sannan
ta tsaya cak ta dubi gabas
da
yamma kudu
da
arewa ga dukkan alamu dai
wani
ko wata ta biyo
a
fusace tane neman inda ta shiga
amma
bata gani
ba,don
haka sai ta sake nausawa
cikin
kasuwar da
sauri
ta rinka leke cikin rumfuna da
lunguna
lunguna
na
cikin kasuwar.Dukka da cewar
taga
jama'a sun
biyo
bayanta da yawa ko kada bata
damu
ba,itadai
kokarinta
shine taga wanda take
nema
ruwa a jallo
amma
ko alamunsa bata gani
ba.Al'amarin
daya
dugunzuma
hankalinta kenan.Koda
taga
ta karade
kasuwar
gaba dayanta har tsawon
kusan
sa'a daya
da
rabi ba labari kuma jama'a sunyi
cincirindi
a
bayanta
sai ranta ya baci ainun
bata
san sa'adda ta
yunkura
ba ta kurma uban ihu mai
tsananin
firgitarwa
tane mai zare
takobinta.Kafin
kace wani
abu
tuni an tattake kayayyakin
jama'a
tamkar yaki
akeyi
kuma kowa ya watse
kasuwar
tayi tsit tamkar
mutuwa
ce ta gifta.Tsananin shirun
daya
wanzu ne
yasa
jarumar ta jiyo sautin
numfashin
mutum a cikin
wani
dogon durum na karfe wanda
ke
cike da
ruwa.Saidai
wannan ruwan durum
ruwane
na
kazanta
wanda ake wanke
kwanukan
abinci dashi a
kusa
da rumfar da ake siyar da
abinci.Koda
jarumar
ta
jiyo numfashin mutum a cikin
wannan
darum sai
ta
daka tsalle sama ta dira akan
durum
din tana mai
raba
kafafunta a kansa duk da
cewar
bakin durum
din
siriri ne matuka amma ko
girgidin
faduwa batayi
ba.Kawai
sai ta sunkuya ta tsoma
hannunta
cikin
ruwan
take taji ta kama gashin
mutum
ai kuwa sai
ta
fincikoshi sama ya na kwala ihu
sakamakon
tsananin
zafi da zugin da yaji.Take
ta
kwalashi a kas
yana
jike sharkaf ya sake kurma ihu
a
lokacin yaji
kamar
kashin bayansa ya karye ba
wani
bane face
matashin
saurayi dan kyakyawa
wanda
shekarunsa
bazasu
haura ashirin da uku
ba.Koda
wannan
saurayi
yaga wannan jaruma ta
dirfafoshi
rike da
takobi
tsirara sai ya zube kasa a
gabanta
ya kama
tuba
yana cewa tayi masa rai.A
lokacin
da jikinsa ya
kama
kyarma a daidai wannan
lokaci
ne mutanen
kasuwar
suka fara dawowa,nan da
nan
suka taru
wajen
sukayi musu kawanya suna
kallon
abinda ke
faruwa
cikin al'ajabi.Budurwar
ma'abociyar
kwarjini
ta
iso daf da saurayin ta dora kaifin
takobinta
akan
wuyansa
take gumi ya karyowa
saurayin
sa'adda yaji
kamar
ya saki fitsari a wandonsa
sannan
ta dubeshi
tace,ina
abinda ka sata a cikin jakar
guzurina?Jikin
saurayin
na kyarma ya zura
hannunsa
cikin aljihun
wandonsa
ya fiddo wata guntuwar
jemammiyar
fata
wacce
ke nannade yamika
mata.Cikin
hanzari
budurwar
ta amshe ta bude jakar
guzurinta
tasa a
cikin
sannan ta cire kaifin takobinta
daga
kan wuyan
saurayin
koda ganin haka sai
saurayin
yayi doguwar
ajiyar
zuciya kuma fuskarsa ta
fadada
da murmushin
murna
bisa ganin cewa jarumar ta
kyaleshi
bata
kashe
shi ba kawai sai ya mike
tsaye
zumbur ya
juya
da baya ya falfala da gudu
izuwa
wani bangaren
daban
na kasuwar yana cikin gudu
ne
yaga wannan
budurwa
jaruma tsulum a gabansa
cikin
tsananin
kaduwa
yayi tirjiya a gabanta ya
dubeta
cikin alamun
tsananin
tsoro yace,tundai na baki
abinda
na satar
miki
kiyi mini rai don girman
iyayenki
kada ki kashe
ni.Koda
jin haka sai jarumar tayi
masa
murmushi
lokaci
guda kuma ta murtuke
fuskarta
tace,ba
kasheka
zanyi ba amma dole ne ka
amsa
wadansu
tambayoyi
daga gareni tunda kana
biye
dani tun
daga
birnin Misra har izuwa nan
birnin
Yamein,kasashe
uku muka ketare
ta
cikin teku duk
jirgin
da nashiga kaima saika shiga
ashe
akwai
abinda
kakeso a wajena?Ina da
kudade
masu yawa
a
cikin jakar guzurina amma ko
dinare
daya baka
dauka
ba sai ka dauki abinda yafi
dinaren
daraja
kuma
yafu duk wata dukiyar a
wannan
duniya.Dole
ne
nasan dalili kuma nasan wanda
ya
turoka
watakila
sanin hakan ya kaini ga
samun
nasarar
gano
inda nake nema.Koda wasa
kada
kayi tunanin
guduwa
daga hannuna ko kuma
kayi
mini karya bisa
abubuwan
da zan tambayeka
domin
yin hakan
daidai
yake da siyar da
ranka.Kasani
zan iya
shaftare
makogwaron bil'adama da
kaifin
takobina
kamar
yadda kullum ake yanka
kaza
ko naman miya
a
kasuwa,ni da kai duk nasan cewa
muna
jin yunwa
don
haka ka biyo ni muje mu nemi
abinci
muci
domin
mu sami nutsuwa.Koda
gama
fadin hakan sai
jarumar
ta juya ta nufi cikin kasuwa
cikin
razana da
dari
dari saurayin ya bita a baya
kamar
ace kyat ya
saki
gudawa a wando,su kuwa
jama'ar
kasuwar
wannan
karon sai aka rasa wanda
zai
sake bin bayan
wannan
budurwa saboda an
razana
da ita ainun bisa
ihun
da tayi a wancan karon wanda
ya
zamo
sanadiyar
tarwatsa kasuwar gaba
daya.Kai
tsaye
jarumar
ta nufi rumfar wata mata
mai
siyar da abinci
jama'a
suka rinka ratsewa
¶Abubakar
Haleefah Physicist¶
suna
bata hanya har suka shiga
cikin
rumfar ita da
saurayin
suna shiga sai gaba dayan
jama'ar
dake
zaune
bisa kujeru suna cin abinci
suka
tarwatse
suka
gudu suka bar abincinsu
alhalin
basu gama ci
ba,wasu
ma anan suka bar
takalmansu
da yan
kayayyakinsu.Ita
kuwa matar mai
rumfar
sai ta
durkusa
kasa bisa guwiwowinta a
gabanta.Matar
tace
kiyi mini zan baki gaba dayan
cinikin
yau.Koda
jin
haka sai jarumar tayi sauri ta
kama
kafadun
matar
ta tashe tsaye ta dubeta
cikin
alamun
tausayawa
tace,ni ba yar fashi bace
abinci
mukazo
mu
siya muci kuma sauran
kwastomomin
kima da
suka
gufu basu biyaki kudade ba
sakamakon
firgita
dani
zan biyaki kudin abincinsu,ki
kwantar
da
hankalinki
ni ba mai cutarwa
bace.Koda
gama fadin
hakan
sai Jarumar taje ta zauna a
kan
wata kujera
dake
karkashin wani tebur mai
kujeru
biyu
kacal,shima
saurayin sai ya zauna
tare
da ita amma
har
a sannnan akwai alamomin
tsoro
a tare
dashi.Mai
abincin ta dubi Jarumar
tace,ya
shugabata
wane
irin abinci zan kawo miki?
Jarumar
tayi
murmushi
tace suna na Yazirina bin
Salmara
karki
kara
bani girma domin nida sarauta
ko
wata
daukaka,shinkafa
da kaza zaki
kawo
mini amma shi
abokin
tafiyar tawa bansan abinda
yake
so yaci
ba.Cikin
nutsuwa mai abincin ta
dubi
saurayin tace
kai
kuma fa?Saurayin yayi
murmushi
cikin yake yace
suna
nan Mujahid Ibini As Sudusi
nima
ki kawo mini
irin
abincin da abokiyar tafiyata ta
bukata.Koda
jin
haka
sai Jaruma Yazirina ta yiwa
Mujahid
wani irin
murmushi
na mugunta tace wato
kaga
banza ta fadi
ko
zaka kwashi bati shine kai ma
kace
a kawo maka
kaza
to kasani bayan cin kaza
akwai
cin kwakwa a
gaba.Cikin
razana Mujahid ya zaro
idanu
yace me
kike
nufi da cin kwakwa?Yazirina
tace
karka damu
lokaci
zai baka amsa.Nan da aka
kawo
musu
shinkafa
da kaza dafaffiya kowa
farantinsa
daban
kuma
aka kawo musu ruwan inibi a
cikin
tambula da
kofuna
guda biyu suka kama kintsa
cikinsu.Muhajid
ya
bude cikinsa yayi ta zuri har
saida
ya koshi yayi
gyatsa
amma duk da haka bai rage
ko
fiffiken kazar
ba
duk da cewar kazar katuwa ce
sosai,sai
mutum
yana
da matukar cin abinci yake iya
cinye
rabin
wannan
kaza.Ita kuwa Yazirina
kaso
daya cikin kaso
hudu
na kasar ta cinye shinkafar
ma
cokali uku tayi
kawai,itama
kanta tayi mamakin
yadda
Mujahid ya
cinye
gaba dayan abincinsa.Nan
take
Yazarina ta
bude
jakar guzurinta ta fiddo da
kudi
ta biya abincin
da
suka ci ita da Mujahid sannan ta
biya
na
kwastomomin
da suka gudu kamar
yadda
tayi
alkawari,kawai
sai ta dubi Mujahid
tace
zo mu
tafi.Maimakon
Mujahid ya bita da
sauri
sai ya tsaya
yanason
ya tambayi mai aminci
yace
ta bashi wani
abun
daga cikin kudin da Yazirina
ta
bata,kawai sai
yaji
Yazirina ta kamo wuyan rigarsa
ta
baya ta
fincikoshi.Ba
shiri ya bita a baya da
sauri
suka fice
daga
cikin rumfar,Koda ganin haka
sai
mai abinci ta
daka
tsalle sama ta kama rawa
saboda
murna bisa
ganin
cewa kudaden da Yazirina ta
bata
yau yakai
adadin
cinikinta na mako
guda.Al'amarin
daya baiwa
Mujahid
mamaki kenan ya dubeta a
dan
tsorace
yace
wai shin ina kike son zaki kai
ni
ne?Ni fa ban
san
ko ina ba a garin nan kuma
bansan
kowa
ba.Koda
jin haka sai Yazirina ta juyo
a
fusace ta
cakumi
wuyan rigarsa da hannu
daya
ta dagashi
sama
sai gashi kafafunsa na wutsil
wutsil
a sama
tamkar
sillan kara ta daga,sannan
ta
daga kanta
sama
ta dubeshi tace,Kai tsohon
barawo
kada ka
rainan
hankali,gaba daya kasashen
dake
nahiyar nan
kasan
cikinsu da wajensu kamar
yadda
kasan
yunwar
cikinka saboda
kwarewarka
a iya sata.Kana
zaton
bansan ka bane?Kaine ka
sace
hular sarautar
Sarki
Atman Bin Ka'ab na birnin
Kisra.Kaine
ka sace
dukiyar
attajiri Katadata bin Al
Aswad
na birnin
Sham
kuma kai ne ka sace lemar
sarauniya
Iklaira
bin
Aslam ta birnin Hindu kuma
Boka
Kaisu Bin
Alkama
ya baiwa dukkan
wadannan
abubuwan
uku,ya
biyaka ladanka yau kusan
shekara
biyar
kenan
kana aiki a karkashinsa yana
baka
sa'a akan
sana'arka
ta sata.A halin yanzu duk
fadin
duniya
babu
wani barawo daya kaika
shahara,dauka
da tarin
dukiya.Tana
gama fadin hakanne
sai
ta dire shi
kasa.Lokacin
da Jaruma Yazirina
tazonan
a
jawabinta
sai gumi ya tsatstsafowa
Mujahid
saboda
tsananin
mamaki da firgitar da yayi
saboda
yanzu
ne
ya tsorata sosai da Al'amarin
Yazirina
ya gane
cewa
tabbas ta cika shu'umar
bokanya
domin in
bata
kasance haka ba babu yadda
za'ayi
tasan duk
wannan
sirri nasa....
08161272634
TASKAR
AJALI.1
LITTAFE
NA DAYA
PART
B.
type
AA MISAU.
POST
SULEIMAN ZIDANE KD.
WHATSAPP
09064179602
ta
baya ta
fincikoshi.Ba
shiri ya bita a baya da
sauri
suka fice
daga
cikin rumfar,Koda ganin haka
sai
mai abinci ta
daka
tsalle sama ta kama rawa
saboda
murna bisa
ganin
cewa kudaden da Yazirina ta
bata
yau yakai
adadin
cinikinta na mako
guda.Al'amarin
daya baiwa
Mujahid
mamaki kenan ya dubeta
a
dan tsorace
yace
wai shin ina kike son zaki kai
ni
ne?Ni fa ban
san
ko ina ba a garin nan kuma
bansan
kowa
ba.Koda
jin haka sai Yazirina ta
juyo
a fusace ta
cakumi
wuyan rigarsa da hannu
daya
ta dagashi
sama
sai gashi kafafunsa na wutsil
wutsil
a sama
tamkar
sillan kara ta daga,sannan
ta
daga kanta
sama
ta dubeshi tace,Kai tsohon
barawo
kada ka
rainan
hankali,gaba daya kasashen
dake
nahiyar nan
kasan
cikinsu da wajensu kamar
yadda
kasan
yunwar
cikinka saboda kwarewarka
a
iya sata.Kana
zaton
bansan ka bane?Kaine ka
sace
hular sarautar
Sarki
Atman Bin Ka'ab na birnin
Kisra.Kaine
ka sace
dukiyar
attajiri Katadata bin Al
Aswad
na birnin
Sham
kuma kai ne ka sace lemar
sarauniya
Iklaira
bin
Aslam ta birnin Hindu kuma
Boka
Kaisu Bin
Alkama
ya baiwa dukkan
wadannan
abubuwan
uku,ya
biyaka ladanka yau kusan
shekara
biyar
kenan
kana aiki a karkashinsa yana
baka
sa'a akan
sana'arka
ta sata.A halin yanzu duk
fadin
duniya
babu
wani barawo daya kaika
shahara,dauka
da tarin
dukiya.Tana
gama fadin hakanne
sai
ta dire shi
kasa.Lokacin
da Jaruma Yazirina
tazonan
a
jawabinta
sai gumi ya tsatstsafowa
Mujahid
saboda
tsananin
mamaki da firgitar da
yayi
saboda yanzu
ne
ya tsorata sosai da Al'amarin
Yazirina
ya gane
cewa
tabbas ta cika shu'umar
bokanya
domin in
bata
kasance haka ba babu yadda
za'ayi
tasan duk
wannan
sirr
0 Comments
Post a Comment