Kwana Ashirin Da Daya
Yarinya ce kyakkyawa ke tafiya akan hanya, yarinyar wacce taci sunanta Hanifat, tabbas idan kagan ta zakace da ita ‘yar asalin larabawa domin tin gurin tsarin diresin ta bambanta da sauran mata ‘yace mai tsantsan ladabi da biyayya a gun nagaba da ita.
          Yarinya ce mai yawan hakuri da kuma tawali’u ga dukkan abinda ya faru da ita ‘yace mai tausayi ga kuma rikun amana, agurin kyawtawa iyaye kuma ba sai nace komai ba.
“Yan Mata Jimana, ko bakya jina ne? ki saurareni kiji me nake fada”  a dai-dai wani gungu ne na gayu ta iso, da yake na sanarda ku cewa ‘yace mai tarbiyya sam bata kula suba. Ganin hakan Gayen ya tashi a inda yake zaune ya bita ya cigaba da surutan sa, ita kuwa sam bai ishe ta kallo ba.
Hanifat ke ce wa, “Dallah malam kayi hakuri, idan har kana so kayi magana dani ba akan hanya ya dace da ka tsaiyar dani ba, idan har kai mai mutincine ta kuma lura”
“To na naji amma naso na san sunanki” Fadan Musbahu ke nan
Hanifat ta tambeshi tana mai cewa, “Sunana kuma?
Musbahu ya ce, “Eh mana”
Dawane dalilin kuma kake neman sanin sunana? Samira ta ce hakan.
Musbahu ke cewa, “ban gane ba, eh to naji bara kiji dalilin”
Dan Allah kayi hakuri baran tsaya ba, kuma Dan Allah kayi kadaina biyana hakanan” Kaji ‘yar digan mutin ci Samira kenan.
“Haka kika ce? Bamatsala ni zan koma sai wani karon. Bye for you”. Musbahu ke wannan zancen agareta.
          Ya tafi abinsa  da ficewan sa, ya garzaye sai gun abukansa. “Musbahu ya akayine”?ba asami nasara bane”? Ishaq ya ce hakan. “Babah  kawai share, wallahi ni ban taba haduwa da ‘ya dibgaggiya kamar wannan yarinyarba, to wazata munawa cewa ita ustaziyace?, ai wannan zancen kawaine  wallahi” Ishaq ya bude bakin sa yana cewa, “Musbahu karka damu ai wannan ba wani abu bane, Just kept silent don’t worry, Insha Allahu za ka ga me zai faru da ita” “Haba Broz gaskiya kake fada kuwa? Duk da ya ke nasan kai bakkada wasa wallahi.Fadan Musbahu kenan. Nan ta ke suka lale gaba dayan su suka wace a dabar.
BAYAN WATA DAYA, Yaro! Dan Allah zo na aika ka agidan nan, aika Yaron keda wuya, zance da ku tin yaron bai fito ba,  sai ga Mahaifin Hanifat ya fito. Musbahu ya gurfana yana mai cewa, “Baba banka da wuni, ina fatan kuwa lafiya” Mahaifin nata ya amsa masa da cewa, “Lafiya kalau wallahi, amma daga ina haka; Musbahu ya amsa ya na cewa, “Eh! Dama na ga ‘Yar gidan ka ce, sai naga abin da yafi da cewa na zo na tarar da kai na sanar da kai.
Faman susan kai ya ke idan kaganshi kace da gaskiya ya ke yi. Mahaifin nata hakan ya matikar faran tar da ransa, bashakka da kaga wannan tabbas ne kabashi shaidan cewa dane mai halin kirki, dane kuma Nagari, saboda irin halayen sada suka nuna azahiri.
“Da yake dai ban tambiyika sunan naka ba, Mahaifin Hanifat ya ce hakan. Sunana Muh’d Awwal fadan Musbahu ke nan, kai Allah ya saukake mana idan kaga mutum azahiri zakace tabbas na Nagari ne amma ina ko me yake nufi Allah shine masanin wannan, amma muzuba kawai mugani shine abin da zai iya sa mu fahimci ma’anar da yake acikin zuciyar sa.
Lallai Muh’d Awwal… eh! amma kaganta ne? ku ka… kamun Mahaifin nata ya idar da maganar sa, ya yi hanzarin katse shi da cewa, “Haba Baba taya zanga yarinya batare da na ganka ba, ai wannan kamar ya nuna rashin tarbiyya da kuma rashin gimamawa ga iyaye, ai hakan sam bai dace ba, har na tsayar da yarinya akan hanya sam Baba wannan baidace agareni ba, kuma ya zamu zubarda mutinci na iyaye da kuma zubar da mutincin kaina da nata kaga kuwa hakan sam baidace ace kamar ni na aikata wannan ba. kasha zancen Musbahu. Mahaifin Hanifat ya ce “Kai amma ka na da sanin ya kamata” ya sake yana cewa, “duk da ya ke basai na tsayar da kai ina yi maka dugun bincikeba, bara na je na kira maka ita kugaisai”. Kaji zance Mahaifin Hanifat kenan. Amma kash wani hanzarin  ba guduba Mahaifin Hanifat ku na ce daku Alh. Isma’il ya yi kuskure Babba da ya ke sam bai kawo tinanin cewa ya tambiye shi da cewa shi dan waye ne, amma ma’iya cigaba da muji me zai iya aukuwa nan gaba. 
Bayan ya kira mar da Hanifat suka gaisa sam-sam bai yi wani daukan lokaci ba yay mata sallama ya tafi abinsa, duk da ya ke kasan hausawa kan ce mai lababe baya tayar da hanninsa.
Akwana a tashi, hakan ne suke a tare har soyayyar ta kai su da dayan baya iya juriyar rashin ganin dayan dan uwan sa, soyayyar su tayi matikar karfin gaske, zan iya ce da kai/ki Hanifat da ta zirfafa a so.
Bayan wa’ansu kwanakin masu yawan gaske, Hanifat ce ta re da Ishaq a zaune acikin wani dan lambun gidan na su, firan na su yayi matikar nisa, acikin firar ne Ishaq ya ke cewa, “Hanifat ina so nasanar dace da wani abin wanda nasan ke bakyada masaniya akansa” Hanifat ta ke cewa, “Ishaq menene kuma wanda idan gance ka da banda masaniya akansa?” “To yakan yo kisan wanda ike a zahiri amma ai nasan bakyada masaniyar wanda ike a badini, dan haka sai ki saurareni kawai kiji nenake nifi, ko kuma mezan fada. Hanifat take cewa, “Ina saurara”.
Budan bakinsa ya fara da cewa, “Hanifat ina mai sanardake cewa shi so wanda yake na gaskiya  azahiri zaki iya ganewa amma sam a ganina bada lora da irin sonda nake maki, “Ban bangane ba, kamar ya kake nifine? Hanifat tace hakan.“Au to ke me kike nifine? Ya kamata ace kitsaya ki saurareni mana, wani sa’ilin kya iya fahimtar maganata”. Duk dayake Hanifat battada masaniya me yake nifi da wannan zance, amma kawai ta yimar wannan ne badan komaiba, kawai tana sone da wasa mar da kwakwalwa ne.
Zatun shi ta dago hannu ne, nan take ya sauya maganar, ya cigaba ya cewa, “Hanifat Kaunar ki ce tamamaye zuciya bashakka kece wacce na baiwa amanar kaina, Hanifat ki rikani amana, karki kasance mai zubarda mutinci na, kuma karki kasance mai zubarda soyayyata.
Bashakka ke ‘yace tagari kuma ke ‘yace wacce takasance mai riko ga addini, ‘yace ke mai asali, ma’ana ce ‘yar jincice Nagari. Hanifat na kasance mai baki ragamar soyayyata, kikasance mai tallafi a gareni. Kaunarki ce kawai a zuciyata, sam-sam ni bansaka wata ‘ya mace wacce zata maye gurbinki ba, kece kadai a gabana. Fatana kikasance mai tallafi agareni. Yake ‘yar digan mutinci, har kullin soyayyarki dada yaduwa takeyi a zuciya bashakka kece wacce nabaiwa rayuwa ina sonki ina kuma kaunarki har kullin kaunarki ce azuciya dare da rana. Alokacin da yake wannan zancen bashakka idan ka ganshi tillas ne tausayinsa ya kamaka.
Hakan ya matikar kara chusa soyayya azuciyar Hanifat gabadaya tausayinsa ke kwararowa, ta rasa irin amsar da zata iya bashi, kawai ta yi wani ajiyar zuci ta dan duna kanta a kasa. Jim kadan take cewa, “kar ka damu Insha Allahu zan kasance mai share kukanka, nakasance mai riko da soyayyarka, harkullin zankasance sanadin farin cikinka, ina sonka ina kuma kaunar ka, har abada.
BAYAN MAKO UKU “Umma Ishaq ne yace ko zai iya ya turo Mahaifahsa? Kusa da Umman ta take a zaune a lokacin da take wanna zance. Hanifat manyam mata ku kunya bakyaji dan kanki kike wannan zance”.To Umma meyene na kunya kuma?” Hanifat ta ce hakan. Mahaifiyar ta tayi murmushi ta ce, “Idan Abban ki yazo zan sanar dashi. Murmushi kawai Hanifat ta yi.
BAYAN KWANA BIYU “Ishaq kasan meke faruwa ne? inji Hanifat. A’a me ke faruwa kuma?Ishaq ya mayar mata da tambaya shima. “to albishirin ka, Hanifat tace hakan. “Goro” fadan Ishaq, kasan ka aikani da natambaya ma cewa ku zaka iya aikowa da iyayenka”. Eh! Haka ne ya akayi ne? “To Abba ya ce ka iya turowa, abinda ya yace dama yana da niyyar yima wannan zancen. “ko da gaske kike” “zanfada ma karya ne” amsar Hanifat kenan. A’a bance ba.gaba daya su kayi murmushi. Cikin wannan suke sai ga mahaifin nata zai fita, ya yi daidai alokacin Ishaq na gidan. Cikin hanzari da kamun kai Ishaq ya durkusa ya na cewa, “Abba barka da wuni” Mahaifin na ta Alh. Isma’il ya ce, “Alhamdilillah na jidadi kwarai da natarar da kai, domin akwai wata ‘yar magana danake so nayi dakai, idan kaje gida dan Allah ka toru iyayen ka domin ina sone nadan yi tafiya cikin wannan makon. Zance Mahaifin Hanifat kenan.“Ba matsala Insha Allahu zan sanar da su, duk dayake Abba yay tafiya amma nayi waya dashi ya sanar dani cewa dayardan Allah zai dawo acikin wa’annan kwanakin”.“Dama Abban naka baya a gari ne?” Eh! Wallahi dama ya dade dayin tafiyar don inaji yanzin yana da wata tara da yin tafiyar, dama ya tafi Malaysia ne”. sai faman susan kai ya keyi sai kace dashi makaryaci da yake ai karyarce ya ke yi. “Au nima din Malaysia zan je amma ba damuwa tinda ya sanarda kai zai dawo acikin wa’annan kwanakin badamuwa.
Bayan ya wuce Ishaq ya tashi ya kalli Hanifat yayi murmushi, wai ita kunya taji, Hanifat ta rufe fuskarta ta zura aguje ta nufi shiga gida, Ishaq sai faman kiranta yake yi amma taki ta dawo, ya gyada kai ya fice abinsa.
Bayan rabuwarsa da Hanifat Ishaq ya nufi dabarsu da zuwan shi, cewa yake “H!!! Hello guys!, ya yi wani nannade yatsusa kace dashi kuri’ace zai dangwala, kume suke nufi da wannan kawai sai suka lale. Musbahu ya ce, “Takare ya akayine two days kadena shizowa bila”. Musbi kasan yanda abubuwan suke fa kasan ina process na yarinyarnan” Musbahu ya katse hanzarinsa da cewa, “wace kenan?” Ustaziyyar mana ko kamantane? Kai!! Babah ina kyautata zatun ka kaso mana princes? Musbahu ya fadi hakan.“Takwala kasan meke faruwa kuwa? Hadani da kwalbar sirof daya kasha labari babah” Ishaq ya ce hakan.  Kaicu dama bazaka iya shaida na dan adam ba, domin wani sa’ilin zaka iya shaida da cewa lallai wannan mutum - mutum ne Nagari kuma mutum ne mai tawali’u da sanin ya kamata. Amma kawai kana yine abinda ka gani azahiri don haka fatamu Allah hadamu da mutanen kirki kuma Nagari ya kuma samu kasance ashedemu da hallaiyya Nagari amen.
Bayan ya aza kwalba daya ta sirof ko kuma zan’iya ce daku Totolin domin shine abin yayi gun samari ahalin yanzu, duk daya ke kar na cikaku da surutu bara na dura a inda muke dumin cigaba.
Me Ishaq ya fara da cewa bayan daukar caji, “Musbi kasan abinda muke aciki ahalin yanzu?” a’a so nake nasani mana, fadan Musbahu. Cikin kankanen lokaci Ishaq y asanar da Musbahu duk yanda suka yi da ita kai harma da iyayenta baki daya.  
“Hmm wani ajiyar zuciya ne Musbahu yayi, ya kara da cewa, Bashakka akwai yaki agabammu. Yanzinnan meye mafita agaremu?”Dayake ishaq ashirya yake ga dukkan abinda zai fada, kuma yanada mana sananiyar duk abinda ya aikata bazai bashi ruwaba a nashi Nazarin/Tinani.
Bude bakinsa keda wuya yake cewa, “Musbi karka damar da rayuwarka da ya ke nagayama da cewa ni mai baka mamaki nan gaba, amma ina neman alafarma daya gunka”.
Nana take Musbahu yake cewa, “wane irin alfarma kakeso duk duniyar yanzunnan za’ayima my Friend, don’t worry just tall me.
Ishaq ya dan taboshi ma’ana ya dan taro kunnesa yaji, Bayan kamala maganganun da ishaq ya sanar dashi, nan take suka dauke kuwa suna faman tsalle ce kake wa’anda aka yi wa busharar da Aljanna tun anna duniya. Bashakka daganin irin wannan ka’iya dago hannin cewa tabbas ba alkhari bane suka kulla.Duk da ya ke muma kammu bamada masaniyar menene manufar wannan, amma ma’iya cigaba da biyan kididdigi domin gano menene manufar wannan.
Idar da wannan zancen keda wuya Ishaq ya dakku wayar sa acikin aljihun rigarsa na gaba ya dinga wani latse-latsen wanda yake wata kila zamu iya gano menene sanadin yin wanna. Bayan ya kammala Ishaq da Musbahu su ka lale irin wannan wanda suka saba. Kai gaisuwar ma idan ka ganta kace dasu fada suke yi, domin irin yanayin gaisuwar.
Rabuwansu ke da wuya sai ya zarce a gidan su Fatima da isarsa, yayi da ce da fitowan ta. “A’a manya-manya ba’ammana hijiraba, duk da bilar ma zance kadaina ziyara, ina fata lafiya ya kawo ka” Eh! Tima