WASALI DAYA
SIN ONE (1)
Da karfe tara na safe Alhaji Yusha’u baban salima yafito da ga kuryar
dakinsa izuwa falo da jakarsa tazuwa office arataye alamar ya kammala
shirye-shirye zaije wurin aiki, turo kofar falon da yayi ke da wuya sai yaci
karoda hajiya a’isha matarsa zaune a falo tana jiran fitowarsa tayi masa rakiya
ko adawo lafiya. Wato mamar salima a’a hajiya yau zaman rangadi kawai akeyine? Hmm
baban salima kenan ai wayon da kake yimin ne nagaji dashi na lura kwana ukun
nan koda nake Ankara ka fice abinka ba tare da nayi tozalin safeba ko kuma
insamu ladar adawo lafiya ko ta rakiya mamar salima ta fada acikin yanayi na
shagwaba ga mai gidan nata Alh. Yusha’u acikin yanayi na murmushi da kuma kada
kai baban salima yace da ita Aisha bakya barin zolaya wallahi .wai ina salima
ne yau bata fito bane har yanzu? Wallahi makare ta tashi yanzu take sallah,
inji Aisha haba wannan wane irin shashancine haka sallar safe karfe tara Aisha?
Ya fada acin yanayi na damuwa bayan da yayi shiru na Kamar kika daya ya sake
nisawa yace amma dai kin gaya mata sakonako? Eh. Nagayamata yan zuma jiran nake
ta fito inkara nanata mata don ba gajiya akeba Aisha ta acikin ladabi ga
mijinta wato yusha’u. to shikenan ni zan fita to adawo lfy mai gidana Aisha ta
fada acikin farin ciki.
SIN TWO (2)
Aisha:-Salima:-Salima!! Hajiya Aisha
ce mamar salima zaune a falo rikeda rimot yayin da take kokarin raba hankalinta
biyu daya awuri kunna talabijin bango (plasma) daya kuwa awurin kiran yar tata
salima na am momy wannan itace amsar da
tayiwa mahaifiyar tata amatsayin amsar kiran da tayi mata, batare da saba
lokaciba kuwa tafito jikinta asauyaye bisaga sanin cewa gatanar gizo bata wuce
ta kokiba maganarce dai daya da aka saba ko yanzu itace za’ayi zamanta keda
wuya akan dayar kujerar dake fuskantar ta mahaifiyarta acikin katafaren falon
gidan ne hajiya Aisha ta soma gayamata salima: wai ina zancenmu ya kwanane
kingafa ko yau da abbanki zai fita sai da yayi wannan maganar tukuna yafita.
Salima:- Wallahi
Umma nidai abba yasani a gaba wai meye haka shin mutum kulum baza’abbarshi ya
hutaba ta fada acikin shagwaba
Aisha:- Iyeh! Lallai salima wuyanki
yai kauri harma wani antakura maki kike gani ko? Laifi nane nida nake kakkareki
awurinsa amma dagayau zan dinga barinki dashi ki ji irin tsuwar da nake ji
akunnuwana wata kila kyasan dawa ki ke yi.
Salima:-kai! Umma don Allah kirufa
min asiri salima ta fada acin fargaba taredadora hannuwanta acikin labban
bakinta yayinda bakin yake hangame alamar mamaki.
Aisha:- eh mana don naga hakan kikeso
ayi ko?
Salima:- a’a Umma kinga wasa nakeyi
don Allah kiyi hakuri karki gaya masa tafada acin yanayi na karaya da damuwa.
Aisha:- To inkuwa ba hakaba kiyi
kokari fito da mijin aure a kwanan nan a tsayar da Magana guda daya. Kinji na
gaya miki.
SIN THREE (3)
Na’imaacikin dakinta na kwana a
gidansu yayinda take kan gado ta tashi banta da filon dake kan gadon wato ta
kishingida akan filon data jingina akan jikin gadon idanun ta kuwa a kafe a
sama alamar tana cikin halin nazarine kamar daga sama taji wayarta tayi ringing
wanda shine ya katse mata nazarin da takeyi takuma mika hannunta asauyaye ta
dauko wayar tata taga ashe kawarta salimace ke kiranta adaidai lokacinda ya
dace ace tana can sharer bacci harda mishari azawar datayi a kunnenta taji
muryar salima nan take kuwa tace da ita ke kuwa me ya hanaki baccine
Salima:- Abinda ya hanaki domin na
tabbatarba haka kawai kika kai karfe goma sha daya bakiyi bacciba.
Na’ima:- wallahi salima Ummace ta
sakani a gaba wai dole saina fito da mijin aure a kwanan nan.
Salima:- wallahi na’ima duk matsalar
dayace nima abba ya takurani saina fito mijin aure
Na’ima:- Aikuwa da kinyi jinkiri
kadan da nice zanfara kiranki domin kuwa wallahi na rasa abinda yake yimin dadi
arayuwata ammafa kinsan wannan baisani na janye kudurina da nake akai.
Salima:- kawata ai biyan bukata yafi
dogon guri inji kuda wallahi nima bazan karayaba saidai kome za’ayi ayi amma salima sai salim
aduk inda yake aduniya
Na’im:- Allah ya barmin ke kawata
haka na’ima sai na’im saida safe kawata
Salima:- Allah ya nuna mana.
SIN FOUR(4)
Na’im da salim ne azune awani lambu
na farfajiyar gidan nasu suna cin abinci
akan wani dan wani dan teburinda aka shiryashi domin cin abinci ayayin
irin wannan zaman.
Bayan da na’im ya soma kai abinci
abaki yace yaya na’im har yanzufa kaki motsawa balantana kabana guri inkasa
hajata.
Salim: nakamar meyefa Salim ?
Na’im: haba yaya zancen Aure mana
Salim: murmushi tare da gyadakai
acikin sautin hmm Na’im waikai meyasa kake son tayarda zaune tsayene Aurefa da
kake gani horewace ta Allah kuma da shi da mutuwa duk ba a tsallake lokacinsu
idan yazo kawai mudai kara jiran lokaci
Na’im: haba waikai wane irin lokacine
kake jira haka wanda bairiga yazoba yaya ?katunafa mun kammala karatu kuma
gwargwado munada ayukanmu ahannu to meye kuma yarage ?
Salim: salim da Na’im su mallaki
salima da Na’ima
Na’im: Hmm yaya kenan waikai har
yanzu kanan da wannan tsohon ra ayin azuciyarka karka mantafa yau shekaru uku
kenan dakare karatunmu dasu kuma bawata yarjejeniya ce tsakaninmu dasuba ta
aure hasalima kolam bobbin wayoyinsu bamuda suma haka kuma bamu san indasukeba
basusan inda mukeba kuma ma matsalar anan itace ba mamaki yanzu sunriga sunyi
aurensu agaskiya kawai yaya kadai sake tunani kainefa babba agareni tokuma
yaushe zaka tsaya jiran gawon shanu
Salim: murmushi wai Na’im kodai kaine
kake yimin zagon kasa awurin Abba yake neman dasa keyata agaba dangane da
wannan zance ?
Na’im: haba yaya ni ai bana wan nan
kuma kasani kawaidai tunaninmu dashine yazo daya ya fada acikin yanayin
annashuwa
FADE
SIN FIVE (5)
Na’ima: wallahi salima ba karamin
sakaci mukayiba nazama da mutanen nan amakaranta daya har shekaru uku amma
mukakasa kulla hudadar komai dasu koda ta musanyar lambar waya kosanin
adireshin juna.
Salima: kedai bari kawai kawata
hakika munyi sakaci bakadanba musammanma da aka gama (Exams) ne yadace ko
lambar wayarsu ko adireshi mumallaki daya amma kunya ta hana sai yanzu ga abin
yana cimana tuwo akwarya munkuwa rasa ina zamu saka kawunammu musami saukin
lamari.
Na’ima: amma ba komai indai da rai da
rabo insha Allahu zamu hadu da su komai daren dadewa.
Salima: to amma bakya tunanin cewa
watakil sun dade da mantawa damu kasancewar ba wata kullalliyar maganace
atsakanimmu da suba balantana muce zaman jiranmu sukeyi harya zuwa wannan
lokaci.
Na’ima: eh don wannan kam gaskiyane
amma airabon kwado baya hawasama kuma shi mai arziki ko akuwara ya saida ruwako
?tafada acikin yanayi na wasar abokantaka da nishadi harma suka tafa hannu da
juna. FADE
SIN (6)
Auwalu ya hadu da salima akanhanya ya
kuma yimata al adarda ya saba ta takokarin
tsaida ita ko ainane domin jadada mata kalamansa nakauna Salima :
salima: wannan itace kalmar da Auwalu ya rinka kyarawa Salima yayinda saida
tayi kamar bazata juyobane dayake ta dansoma bashi baya dakyar da alamar rashin
jindadi ta matse ta waigo da tsaki tace wai Auwalu mekake nufi danine wannan
naci haka nagaya maka bana iyawa wai anaso dolene?
Auwalu: Salima aikuwa naci yanzu kika
somaganinsa domin na tabbata shine kadai makullina na bude kofarki ta karfe da
kika kargame afusace
Salima nifa inakara nanata makicewa
itafa soyaya ba kiyaya bace kuma son maso wani koshin wahalane saboda haka
kidaina kallon soyayata afuskar naci kamar yadda naji abakinki isowarsa awannan
gabar kedawuya kuwa sai Salima ta tarbi numfashinsa dacewa dakatta Auwalu ba
wani dogon turanci na tambaye kaba salatin ya isa haka kafadi abinda zakafada
so nake intafi sauri nakeyi karka batamin lokaci kaji furucine kuwa da tayi
acikin yanayin fushi da damuwa fadin hakan tayine kuwa ya bashi damar.
SIN SEVEN (7)
MAFALKIN NA’IMA
Na’ima:
Na’im Na’im haba nawa dan dakata kaji mana kasaurareni kaji me zangayama mana
katausaya mini bisaga irin halin da nashiga wallahi yanzu haka agida iyayena
sun takurani sosai akan cewa saina fito da mijin aure nikuwa naki inbiye ra
ayinsu domin zuciyata tanada nata gurin nadabam hakika Na’im tuni na shar
antawa zuciyata kyamar kowane irin sunan saurayi indai ba mai suna irinnakaba
kasancewar sunammu yazo iridaya wasali dayane ban banci ina fatar zaka karbi
hanzarina.
Wannan
shine majigin Na’ima na Birnin mafarki yayinda taga wani kyakkyawan saurayi mai
irin sunanta atsaye kusaga motarsa maikirar……..yayinda yake kokarin bude gambun
motar tasa domin tafiya wurin nasa sha ani bayan waiwayowar da yayi acike da
mamakine ya furta kalma kamar haka
Na’im:
aikuwa kinyi kuskure domin namiji ko mace duk wanda yake gaugawar yanke irin
wannan sharadin sodadama yake kirkirowa kansa babban aiki
Na’ima:
Na’im dole kafadi haka kasancewar bakasan irin tasirin da nahanga atattare da
hakanba Na’im ka ayyana azuciyarka yaya shawa dakuma dadin sunayen biyu zasu
kasance idan akace sunzamo ango da amarya ? tambayarda kafin ya amsa ta cigaba
da cewa aikaga sunayen sun hadu wasali dayane bambamciko? To yakuma zukatan
zasu kasance idan suka aminta da juna jinsi kawai banbanci ? nantake kuwa Na’im
yayi wani dan saurayin murmushi tare da cewa gaskiyarki Na’ima abin zaiyi shawa
sosai kuwa dahaka sukayi tsaye suka kurawa juna idanuwa kamar bazasu kyaftaba.
SIN EIGHT (8)
FALKOWAR NA’IMA DAGA MAFALKI
Na’imace
kwance akan gado tana yan mirgine mirgine hade dajujjuyakai alamar wadda bacci
ya gundura tana neman malkowa bayan dakika daya sai tasoma bude idanuwanta
kadan yayinda tagane cewa bacci tayi nan take kuwa tazabura firgigi ta tashi
zaune tareda yan sallallami harma datafa hannaye dagakan da tayi zuwa duba
agogon bangone yanuna mata safiya tana daf da wayewa yayinda taga karfe biyar
saura kwata. FADE
SIN NINE (9)
SALIMA TAZO SUPER MARKET
Yayinda
Salima ke kokarin isowa daf da babbar kofa ta shiga super market wato (gate)
anan ta taki daura wato rashin sa argamuwa da Salimdomin shikuwa Salim ya riga
ya shige motarsa yana kokarin rufe kofar motar tasa yariga yagama shoping)
kenan zai koma gida itakuma alokacinne ta iso batako shigaba tukuna Salima
takuwa gane kowanene shi domin sa ardayi bairiga yarufe kofar motarba harma
said a tanisa zata tinkareshine ya jawo kofar yarufe dai dai lokacinda ta kwala
masa kira saubiyu amma bris baikosan tanayiba saboda dama gilashin motar atashe
yake badabata lokaciba kuwa yaja motar yatafi abinsa ba tareda ya fahimci
abinda ke faruwaba Salima kuwa tayi tsaye acikin yanayi na damuwa kimanin minti
daya sai safa da marwa takeyi ranta abace hankalinta atashe.
SIN TEN (10)
SALIMA DA NA’IMA SUNA BAIWA JUNA
LABARI
Na’ima:
wallahi Salima yadda kikaji nagaya mikin nan haka abin yafaru abin takaici wai
saida na falko nagane cewa mafalki nayi ingayamiki takaici ya wani rufeni
narasa abinda yake yimin dadi wallahi adai dai wannan gabarne kuwa Salima ta
tarbi numfa shin Na’ima dacewa hmm aike gwandama naki mafalkine nijiya azahiri
ga Salim inakallonsa amma ahaka ya kubuce mini ba karfi ba dabara kallonsa nake
har bace mani Kalmar kuwa da ta sanya Na’ima saida tazabura kadan acikin yanayi
na nuna damuwa harda kai hannu akirji tace wai don Allah Salima da gaske kike
wannan zancen naki kuwa bayan dan shirun da Salima tayine kafin ta sake cewa
wani abu Na’ima ta sake nisawa tace to garin yaya haka tafaru ?
Salim:
Wallahi in gaya miki dai dai lokacin da nake isa a gun yake kokarin dagawa
harma na soma jarraba laransa amma ina baijiba haka ya tafi a binsa.
Na’ima:
To, amma me yasa kika kasa tare dan acaba kiyi ta binsa a baya har sai kin ga
inane unguwarsu koma kiyi sa’a ya zo ya tsaya a wani gun kizo ki taddashi.
Salima:
Haba kawata kwantar da hankalinki ai indai ana zuwa ruwa bari ake in dai ana
zuwa ruwa bari ake in dai da irin wannan kuren wata rana za a dace.
SIN 11
DA BUDEWAR CAMERA
Mahaifiyar
Na’ima a falon gidan bayan dan nisha din da su kayi ya yin da suka kamala dare
wane Na’ima tace amma Umma agaskiya idan aka yimin haka ba ayimin adalci ba.
Mahaifiyarta:
ai kuwa adalcin ken an a haka ba ita ce yayar ki ba? Kamin Na’ima tace wani abu
sai babar tata tasake cewa yauwa Na’ima wai wanene Na’im? Kalmar da ta sanya
gaban Na’ima ya fada rasi nan take fuskarta ta canza izuwa yanayin damuwa ba
tare da bata lokaci ba ta ce “Umma ta ya kika san wannan suna kuma?
Hajiya
Luba: hmm! Murmushi da kuma gyada kai a hankali, ta yarda kika yi ta famar
sheka mafalki shekaran jiya da dare a cikin bacci ni kuma ina tsaye kusa da ke
komai kika fada a cikin kunne na ya yin da naje tayar da ked a kika ce kina son
za ki yi azumi da naga aki falka shi ne na juyo a bina batare da kin ganni ba
Na’ima:
so ke kai a cikin yanayi na kunya tare dad an murmushin rashin gaskiya
SIN 12
Na’ima
da Salima suna fitowa daga Supermarket ya yin shigarsu Na’im amma ba wanda yaga
wani. Dalili kuwa shi ne, Salima da Na’ima sunga garo matakakan supermarket
dinne a cikin yanayin raha da Nishadi da juna alamar wani abu suka tattauna
wanda ya burgesu har yasa suka tafa hannuwansu a cikin yanayin nasu natafiya
wannan kuwa yana faruwa wane dai-dai lokacin da suka Na’im da Salim ke kokarin
Parking din motarsu daga gefe dayan wajenda ake (Parking) na motoci wanda
sanadiyar hakan yasa babu wanda ya lura da wani a cikinsu bayan karya kwanar da
su Salima sukayi ne kadan saii gasu Salim sun shiga hidimar bude gambun motar
su batare da ba’ata lokaci ba kuwa Na’im day a ke bas hi yake jan motar bay a
zagayo ya tarar da yayansa Salim suma haka su ka shiga yanayin kamar irin nasu
Salima da Na’ima wasa da yanayina koma da ana zolayar juna, wada kane ne amma
kaunar junata sa sun zame kamar abokan juna, ina mada ace abinda suke fada ga
fito zahiri da amshi dariya haka dai suka rike hannun juna suna tafiya har suka
shige a cikin Supermarket din
(FADE)
SIN 13
Salima
da Na’ima suna cikin mota suna hira akan hanyarsu takomawa gida ne kwatsam
Salima ta bude Jakarta don nunawa Na’ima wani abin al’ajabi da ta cikaro da shi
a yanar gizo ta safiyar ranar. Wanda a mai makon dauko wayarce Na’ima taji
Salima ta buga Salati tare da tafa hannayenta harma dacewa na shiga uku Na’ima
na baro waya ta a Supermarket. Direba kaji mu koma don Allah wannan shi ne
abinda Salima ta rinka fada a cikin yanayin damuwa. Ya yin da kawarta Na’ima a
cikin yanayin mamaki t ace da ita tabbi Salima wayace fa! To, inama da labarin
salwancewar rayuwa kikaji ai sai kwakwalwarki ta somar damu. Kuma ai wayar nan
ba bata zatayi ba domin a kudin cikakkun yakinin a Supermarket kika barta kuma
kin tabbatar.
Supermarket
mutanene masu amana komame ka bari indai ananne zaka tadda shi ba tare da
matsalar komai bah aka Na’ima ta ce da ita.
Salima:
hmm! Ke dai bari kawata abin mutum garai shika abki koma da kece fiye da hakama
sai kiyi inji Salima
Duk
kuwa wannan abin da sukeyi diraba baice dasu uffanba, amma yariga ya dauki
matakinsa na komawa supermarket din domin dauko abinda aka manto wato (waya).
SIN 14
DAWOWAR MAHAIFIN SALIMA ALHAJI YUSHA’U DA AIKI
Alhaji:
Salamu alaikum tare da izo gambun shigowa a cikin falon da hajiya Aisha take
yan shirye – shiryen kayayyakin abin cinsa naci dana shaye-shaye akan wani dan
kyakkyawan teburi yaci karo da ita kuwa tsaf irin yadda yake son ganin motarsa
a koyaushe kamin yasake cewa komai sai ta buge da wani dan saurayin murmushi
tare da cewa alaikassalam da kuma sannu da zuwa acikin yanayi na fara’a
Alhaji: Yauwa
a cikin yanayin annashuwa kuma aje jakarsa a gefe dayan kujera da ke gefen
teburin bada bata lokaci kuwa ya kai zaune alamar wanda ya dawo gajiye.
Uwargida rangida hidimomi kawai aketa famayi haka ya fada tare da kura mata ido
kurum babu kyabtawa tsalguwar da tayi saurin yin kallon ne ya sa a cikin yanayi
na shagwaba tace das hi wai meye haka sai kace ni bakuwar kace kamin ya
kankanta murmushinda yayine ta sake cewa dashi gaskiya ni bana so sai barma
kayanka ka hada da kanka in haka ne ta fada ashegwabance Kalmar kuwa da tasa ya
fada a hanzarce ah a’a’a ci gaba da sha’aninki ai ko ba yanzu akwai anjima inji
Alhaji Yusha’u.
Aisha:
Labace baki tare da yin ko oho da batunsa ta cigaba da lamarin gabanta. Bayan
da yadan natsa kanna yace yauwa Aisha wai ina yarinyarnan ne?
Aisha
Sunje supermarket da ita da kawarta Na’ima zasu sayo mayuka dako menene ma suka
ce? Shiriritarsu dai yayin da tayi wata alama da hannu mai nuna sudai suka san
kayansu.
Alhaji:
Wai anya kuwa Aisha bake kike daurewa yarinyar nan gindi akan sagarci ba kuwa
irin wannan yawace yawacenfa bashi da amfani
Aisha:
Wallahi maigida bah aka bane idan yaune dai kawai in ka haifeshi baka haifi
halinsa ba, duk abinda kace ingaya mata na gayamata ni kaina ina yin nawa
dabarun amma duk a banza.
Alhaji:
kinga idan ta dawo kice tasameni aciki ankai karshe dole sai ta gayamin inda ta
dosa damu wannan sakarcin ya isa haka ya fada a cikin yanayi na soma nuna
damuwa
(FADE)
SIN 15
ISOWARSU SALIMA A SUPERMARKET KARO NA BIYU
Salim
da Na’im ke tattakalo mata takala masu hawa kosauka don fitowa daga cikin
supermarket din suka kuwa sun nufi matarsu haikan don su riga sun kamala
siyayyarsu zasu koma gida. Bayan da suka isa awurin motar tasu har sun bude sun
saka kayan da ke rike a hannayensu ne sukatuna da cewa zasu biya har recharging
din Go Tv ya yin da suka yanke shawarar canza hanyar da suka biyo domin saukin
isa a gunda zasu je. Wajen da hakanne kuwa yasa suka sake yin ban hannun makfi
das u Salima ya in da soma (rivers) din nasu ked a wuya sai gasu Salima sun iso
amma dayake ga san motocin duka biyu masu duhune kuma bawanda yasan motar wani
dalilin da yasa barin tasiri kenan. Gama parking din su Salima ked a wuya
Salima c eta daya gafara fitowa a cikin motar a cikin hanzari takuma nufi cikin
supermarket din yayin da Na’ima ta fito a cikin natsuwa ta kuma jingina a jikin
motar da tafito a cikinta amaimakon tabi yar uwartata izuwa cikin super market din bayan
kamar mintuna basufi biyuba sai ga Salima ta dawo acikin anna shuwa wanda
tundaga nesa Na’ima ta yanke hukuncin cewa Salima taga wayarta domin shine
sakon da fuskar Salima ke aikowa Na’ima daga nesa da isowarta kuwa ba tare da
bata lokaciba suka fada mota cike da nishadi da zolayar juna
SIN (16)
Salim
ne a cikin falon gidansu bayan dawowarsu kadan ya ke dudduba jakar hannun da ya
shigo da ita, domin dauko wani (emvlop) mai dauke da hotunan su shi da Na’im,
bayan Na’im din ya shige acikin kuryar gidan. Amma hotuna su kace dauke mu inda
ka ajiyemu, abin kuwa da ya soma sashi damuwa har sai da ya mike a tsaye saboda
rashin sanin meye mafita, kai dan kankanin lokaci ma sai da ya dan soma Safa da
Marwa a hankali a falon tare da damuwa
da kuma tunanin yaya za a yi. Haka dai ya rinka yan sake sake azuci
yarsa, amma ya kasa matsaya daya.
SIN (17)
SALIM NE A WURIN MOTA, NA’IM KUMA YA TARAR DA SHI
Bayan
da Na’im ya bullo waje ne a sakamakon rashin ganin Salim a cikin da ya barshi a
zaune ya kuma hangeshi ya bude gambun motar da suka dawo da ita. Kuma a cikin
yanayin demuwa yana da dudduba cikin tad a alama yana neman wani abune bayan da
yayanke shawarar isowa gun yayan nasa ne ya soma tatta kowa izuwa wurinsa,
isowarsa keda wuya ya ce.
Na’im:
Yaya, meke faruwane? Me kake nema?
Salim:
Hotunan da muka karba ne bangansuba, shi ne nake zaton ko a mota muka barsu, ko
kuma suna a gun kane?.
Na’im:
Haba dai, ka manta hanani ganinsu kayi, kace kai ne zaka fara morewa tukuna. Ko
dai a supermarket din ka barsu ne?
Salim:
Ina zaton haka, idan kuwa haka ne ai dole ne sai mun koma.
Na’im:
A’a ba dai yanzu ba, kaga abinci zamuci tukuna, saboda har ma na fito dashi
naga bakanan, nace bara na duba ka a waje. Kuma mantuwa indai a ____________
supermarket ne ai ba zata salwanta ba, domin su mutane ne masu amana.
Salim:
to, shi ke nan imma dai sun bata da kai ta rutsa, dama ni nasan banyi kyau ba,
kai ne nake tsammanin zakafi haduwa a hoton.
Na’im:
kagafa yaya, duk ba wannan ake ba nifa shegiyarce ta dameni, muje mu gyara kai
tukuna, yazo daga baya muzo a cigaba da wannan zancen.
CUT TO SUPERMARKET
SENCE 18
Salima
da Na’ima camera zata bude a kansu, yayin da suke a cikin matsanancin al’ajabi.
Ya
isheka ganin yanda suka kurawa wasu fotuna da ke ajiye a gabansu a kan teburi idanuwa.
Bayan dan kankanin lokaci kuma, sai ga na’ima tayi wani dan matashin murmushi tare
da kallon kawar tata Salima ta ce, “to, kuma meye wani abin damuwa a cikin
wannan lamari? Ai zai naga nesa ce tazo kusa mai zuwa sama ya taka leda.
Mutanen nan fa nemansu mukeyi ido rufe, sai ga alama ta nuna mun kusa mu
samesu.
Salima:
Haba Na’ima wannan wane irin raggon tunani ne haka? Meye mafita a garemu idan
ya kasance shedanun iskokine suka shigammana al’amari, ko kuwa yau watan
kunyanmu ne zaikai safe, idan ya zamu sirrin da mu kayi shekaru muna boyewa iyayenmu
ne suka gano.
Na’ima:
hmm! To, wai idan ma sun gane sai me? Ai kawai murnace tamu ganin hakarmu ta
cimma ruwa, ko kina da wani burine da ya wuce ki mallaki Salim a duniyar nan.
Salima:
haba na’ima! wannan wace irin maganace? Ai ko na amsa maganarki da eh! Ki dauka
kawai ba a hayyaci na nake ba, domin sanin kanki ne Salim bashi da tamka a
wurina.
Na’ima:
to, idan kuwa haka ne wannan wata damace a garemu a duk sanda iyayenmu suka
sake tunkaromu da maganar aure kawai sai mu nuna musu hotunan samarinmu, kinga
wannan ya isa ya kwantar da hankalinsu kamin mu nemo su a duk inda suke a
duniyar nan. Zance ne kuwa da ya sa Salima a cikin matukar farin ciki, bata san
lokacin da ta tafa hannu da Na’ima ba tare da cewa kawata kinyi gaskiya.
FADE
SIN 19
SALIMA A BAKIN GARKA TSAYE DA AUWALLU SAI FAMAR ZUBA TA KE
YI, MAHAIFIN TA YA TARAR DA SU
Salima:
bayan da ta daga kofar gidan ne ba tare da wata-wata ba ta kyalla idanuwanta
zuwa ga mutumin da ya sallama mata, zaton ta kuwa ya zama gaskiya domin tun
kafin ta fito take nasawa a zuciyar ta wata kilama marar zuciyar nan ne Auwallu.
Cin karo da shi keda wuya sai ta game fuska ta bata rai a lokaci daya ta ce
“Innalillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un, Auwallu kai ne kadai matsalar rayuwa ta
duniya, da zaka mutu da na huta”. Kalmar da ta sa sai da Auwallu ya dafe kai,
saboda mamakin irin yadda Kalmar ta fito daga bakin Salima. Kafin ya ce kala,
ta sake ci gaba da cewa, “Wai kai wane irin marar zuciya ne? na gaya maka bana
sonka, bana sonka, ka fita a haraka ta. In kuwa ba hakaba “in ba hakaba sai me
? nace imba hakaba saime ? Alhaji Yusha’u ne mahaifin Salima ke fada yana
nanatawa domin itace kalmar ta dai-dai gabar maganar ta da ya sharba, ya yin
girsuwar da ya yi mata a bakin garka da Auwallu tana ci masa mutunci ya kuma ci
gaba da cewa, To, ki sani wannan Shashancin an kai karshensa, ya fada tare da
nuna ta da yatsa kin gama naki wargin ni kuma zan soma nawa daga yau. Ya sake
juyawa a wurin Auwallu ya ce, Kai yaro idan da gaske ka keyi aurenta zaka yi ka
toru magabatanka nan da sati daya muyi magana da su. Zancen kuwa da yasa Salima
ta fashe da kuka ta juya a guje ta koma cikin gida.
SIN 20
FLASHBACK
SALIM A SUPERMARKET YANA BINCIKEN HOTONAN DA YA MANTA
Budewar
camera keda wuya sai ga Salim tsaye tare da mai Supermarket ya yin da mai
supermarket ya jinjina kai tare da cewa gaskiya ne, amma abin da ya faru shi
ne. sai ya daga kansa sama ya yi shuru dan wani lokaci, alamar zai tuno abin da
ya wuce.
Nan
take kuwa sai ga Salima ta shigo a cikin supermarket din a cikin yanayi na
hanzari, ba tare da bata lokaci ba ta ajiye jakar hannunta a kan teburin da ke
gaban wannan mutumin mai mu’amalar cinikayya da jama’a. Ta kuma wuce a cikin
sauri da nufi kuryar supermarket din, da yake ita Salima sanannar customer ce
kallo daya ya yi mata ya cigaba da sha’anin gabansa. Bayan da ya soma mayar da
hankalinsa izuwa jakarda ta ajiye ne sai ya ci karo da wani ambuluf zai fadi
kasa a gefen dayan jakar ne kadai ya dafeshi da tuni ya fado kasa. Ganin jakar
a saman ambuluf din sai ya tsammani ambuluf din na mai jakar ne, nan take kuwa
ya dauko ambuluf din ya saka a cikin jakar gudun kar ya fadi a manta da shi
anan. Bayan da ya gama hakaicen labarin ne ya ce da Salim.
Mai
Supermarket: To, kaji yadda abin ya faro
Salim:
To, shi kenan don Allah a kara kulamin sosai ko Allah zai sa su dawo da yake
bada nisa nake ba nan nake a layin nan da ke bayan ku gidan Alhaji Dauda Dan
Kasuwa.
SIN 21
HAJIYA LUBA MAHAIFIYAR SU NA’IMA CE A ZAUNE CIKIN FALON
GIDAN TA, YAR TA SALMA WATAU YAR NA’IMA TA SHIGO
Hajiya
Luba: A’a!, me nake shirin gani haka? Shin ko dai mafarki nakeyi ne? Salma ke
ce ayanzun nan da rana tsaka? Wannan shi ne abin da Hajiya Luba ta fada. Ya yin
da yarta Salma ta izo kofa tare da Sallama da yake kuma sun dade basu gana ba,
wannan shi ne zowarta gida tunda akayi aurenta.
Salma:
Ummah na! Ummah na!! haka ta rika fada tare da shekuwa ta rungume mahaifiyar
tata cike da farin ciki da annashuwa.
Luba:
aw to ina surukin nawa kokuwa ke kadai kika zone ?
Salma:
aa Umma atare mukazo ya tafi ya isarda sakon wani abokinsa ne kawai ya dawo
kugaisa ya ya koma domin ni sati daya zanyi anan “sati daya iye wai abu nayi to
isa ki ajiye jakar kihuta tukuna, “antyna antyna sannu anty Salma yaya hanya shine abinda Na’ima ta rika fada yayinda ta
kwaso gudu ta zo tayi tsalle ta rungumo yayar tata Salma ba tare da tsai
tsayawaba kuwa ta shiga yimata tambayoyi kamar haka
Na’ima:
aw anty salma ina Salmanunki ? ta fada acikin shagwaba da annashuwa
Salma:
salmanuna yananan kalau atare mukazo dashi yananan shigowa bada jima waba,
nadai fahimci suna yennan dadi suke yimaki ko Na’ima?
Na’ima:
to ai sunayen ne sun hadu Antyna kijifa Salma Salman tafada tareda kwatanta yatsunta
na hannaye don kamanta sunayen biyu
Salma:
hmm, lallai, Umma kina jintafa ta fada acikin yanayi na mamaki tareda dora
hannayenta akan lebban bakinta
Hajiya
Luba : tabbi, aike komaima baki ganiba domin kuwa wasali dayannan ba karamin
tasiri yake dashi awurin Na’ima da kawarta Salimaba ayanzu haka ban san inda
taje ta hadu da wani Na’im ba sai famar zabga mafalkin sa takeyi amma koda rana
daya bai taba tako gidan nan da sunantaba.
Salma:
Allah sarki to ai Umma in sha Allahu mai wuya ta kare tunda Allah ya kawoni
yanzu, naki kawai idone don kallo kunnuwa don sauraro damacan mu abokan
shawarar juna ne zo mutafi kanwata Salma ta fada tare da jan hannun kanwar tata
Na’ima suka nufi kuryar daki acikin nishadi mahaifiyar tasu kuwa sai kallonsu
takeyi cike da mamaki yayinda daga karshe tayi wani abu da hannu alamar kudai
kuka sani.
SIN (22)
SALIMA AZAUNE CIKIN FALON GIDANSU TANA KUKAN BAKINCIKI GANIN
CEWA GOBENE AUWALU ZAI TURO IYAYENSA MAHAIFIYARTA TA TARARDA ITA AWANNAN HALI.
Hajiya
Aisha: salima da kuka da rashinsa duka dayane awurinki domin gobece ranar da
gurin mahaifinki zaicika akanki na tarbon iyayen Auwalu da kuma badake agaresu
don haka tarakai kidauki kaddara shine kadai mafita agareki komai ya faru kece
kika jawowa kanki kama da dukan guduma Salima kejin wayannan kalaman da ke
fitowa abakin mahaifiyar tata Aisha yayinda ta game kai da gwiwa zaune kasa
jingine ajikin kujera amarmakon ta haukan kujerar falon anman ko dago kai
batayi ta kalletaba balle harta nuna taji metake fada ahakan dai mahaifiyar
tayi tsaki tashige kawai abinta ta barta anan tanata famar cika aikin da tasa
kanta(kuka )
SIN (23)
SALIM NE ZAUNE AKAN KUJERA YAYINDA AKE GOGE MASA MOTAR DA
YAKE SON YAFITA DA ITA ANA CIKIN HAKAN NE SAI IBRAHIM MAI SUPER MARKET YA TAHO
YA TARADDASHI
A
a Ibrahim kaine tafe adai dai wannan lokacin haka? Kalmar data futo dag bakin
salim kenan bayan ya karbawa ibrahim sallamarsa har suna kokarin hada hannu da
junansu
Ibrahim
eh wallahi nine salim wannan adreshshi ne
mutanenka sukace inbaka idan kazo amaimakon subai hotunan inbaka to
najira kwana biyu naga baka bulloba sai na yanke shawarar na sameka gidda
Salim
kai mutumin yau akwai matsala amarmakon subaka hotunana kawai kabana shi ne
zasu baka adreshinsu kabani menene adreshinsu zai anfanamun?
Karka
damu aiwanan ba komai bane yannada
kyau kaje kaji menene zasu fada ya yiwuma
wannan yazamo sanadi wani alhairin
Salim:
toshikenan babu komai godiya nake malam Ibrahim sai mun hadu ko
Ibrahim:
ok to shikenan nima godiya nake
SIN (24)
Bayan
salima ta dade acikin yanayi nabakin cikiki ne ta yanke sha warar tinkarar
Auwalu domin yimasa magiya ko Allah zaisa tadace , da misalin karfe tara na
safene Auwalu yana zaune a wata farfajiya mai ban shawa akn wata yar karamar
kujera rikeda wani dan karamin littafi ahannunsa yana dubawa kwatsam sai yaji
sallama kamar daga sama ba tare da bata lokaciba kuwa Auwalu ya dago kai don tan
tance gaskiyar abinda zuciyarsa take raya masa nacewa Salima ce tazo wurinsa,
Allah sarki kyallara idanu wansa kuwa keda wuya sai yaci karo da Salima cikin wani yanayi mai ban al ajabi wanda ko kusa
baya tsammanin ganinta acikin irin sa domin kuwa wani murmushi takeyi irin na
kunya tare da tako dai-dai irin na yanayin zaaaaaa babu shakka karim ta yarda
karasowa agunda yake sai da yakasa hakurin ta sameshi a zaune ya mike tsaye ya
tinkare ta shima cike da annashuwa domin ganin yake hakar sa ta cimma
ruwa.haduwar su ked a wuya, acikin alamar za a saita jan rusuna kadan tareda
yimasa kyakkyawar gaisuwa kamar haka:-
Salima:-
yaya auwalu barka day au antashi lafiya?
Auwalu:-
yauwa kanwa ta antashi lafiya ya gidan?
Auwalu
ya amsa mata cike dad a farin ciki-
Salima:-
yauwa yaya auwalu don allah idan baza ka damu ba wata alfarma nazo nema gare
ka.
Auwalu:-
haba kanwata ki daina bata lokacin ki ki fada kawai anga ma meye bazan iya yima
kiba?
Salima:-
auwalu gobe ne iyayen ka zasu zo gidan mu ko?
Auwalu:-
eh! Gaskiya ne wanna karfe biyar na yamma tana bugawa kuwa, ya fada acikin
yanayin nishadi
Salima:-
yaya auwalu kana sona kuwa da gaske?
Auwalu:-
haba kwarai ma kuwa tawa.
Salima:-
to don Allah ina neman kayimin afuwa yaya auwalu kajan ye zowar nan domin zai
iya zama mafarin rasa rayuwa ta.
Auwalu:-
haba meye haka? Me kile fadi ne haka?
Auwalu
ya fada acikin yanayin tashin hankali da matukar damuwa.
Salima:-
auwalu bana sonka! Bana sonka! Bana sonka! Kuma wannan shine gargadin ka na
karshe inkaki kaji to kome ya faru ka zargi kanka kuma wallahi in Abba kasha ni
zaiyi kasani idan iyayen naka suka zo gidan mu a gaban kowa zan cinna wuta in
kona kaina in kona iyaye naka yaso komai
zai faru ya faru adai dai nan ne kuwa ta juya fusace bako sallama ta nufi inda
ta fito a ciki da bakin rai shi kuma
auwalu sai dafe kai yayi hannu biyu acikin takaici da mamaki sai famar kallon
ta yake har ta bace.
SIN (25)
Salma
da kawarta na’ima a falon gidan, budewar camera keda wuya salma ce ta kada kai
a cikin mamaki tace haba na’ima wannan ai akwai waba buna dake da kawar taki
kuna cikin rudani babba. Domin kuwa jiran gawan shanu ku keyi samarin nan fa
basu kosan kana yiba hasalima kudasu ba wanda yasan ina wani yake a yanzu
maganar nan da akeyi;
Na’ima
:- haba aunty salma nafa baki wannan labarin
ne domin ki tayani neman mafita, imfa ba keba duk gidan nan ba wanda
yasan wanna sirrin.
Salma:-
bayan dan suru da salma tayi ne can sai ta numfasa tace tau shikenan bakomai
insha Allahu abu zaizo da sauki tunda har Allah ya sa kun sami hotunan su ta
yiyu idan muka bita hanyarda hotuna suka zo ma iya samun mafita
Na’ima:-
acikin yanayi na tausayi da sagwaba tace don Allah aunty ki taimaka mana kinji.
(FADE)
SIN (26)
Alhaji
yusha”u ne a falon gidan sa ya kasa zaune yakasa tsaye domin yau itace ranar da
yakamata iyayen auwalu su zo, amma gashi har lokaci ya soma kulewa basu zoba
wannan dalilin ne kuwa yayasan yashi safa da marwa ransa abace sai kulla wa
yakeyi yana kwancewa arayuwar sa kamar haka:-
Shin
mutanen na lafiya kuwa kodai dama yaron nan bada gaske yakeyi bane ko kuwa dai
matsala suka samu a hanyar su ta zawa ne?
SIN (27)
Budewar
camera keda wuya sai ga Alhaji dauda ne a falon gidansa zaune a kan wata
katafariyar kujerar da ke cikin kataparen falon. Kai daga nin Alhaji Dauda ba
sai ance maka mai arziki ba ne domin kuwa irin shigarsa kadai ta isa ta
bayyanar da hakan. A gefen fuskantar mahaifin nasa a cikin ladabi da kunya.
Bayan
daukan lokaci kalilan sai ya rufe jarida da ke hannunsa asa adda karkatar
wuyansa ke kokarin komawa gad an nasa Salim ne a cikin manyanci da cikar girma
ya yauwa.
Dauda:
Salim na tabbatar kafin nace komai ka san dalilin da yasa nakiraka to, sai dai
bansan ko Allah Ya sa kadauki matakin kare kanka dag a sharadin da nagindaya
maka kafin inyi tafiya ba, saboda nagaya maka bana tsayi jiran gawon shanu, a
dai-dai wannan gabarne Salim ya shiga shafan kai da Magana a cikin kunya alamar
rashin tafada kamar hakan.
Salim:
Eh! Eh! Am’am Abba Na Na---
Ganin
hakan ne kuwa yasa mahaifin nasa ya katse masa hanzari da cewa
Dauda:
Dakata Salim na fahimce ka bawani katabus da kayi a cikin duk tsibin damar da
nabaka, da yake nag ode Allah da dan cikina na ke Magana wanda yake ya sanni
ciki da bai, baya bukatar tawili ko sharhin maganata in eh. Eh in kuma a’a. a’a
kai ne kafi kowa sanin haka sai dai ka bawa wani labara, to, ka sani kayi wasa
da damarka ta farko da kuma ta biyu, lokaci kuma ya kare ba abin da ya rage
maka. Salim ta yaro kyau ta keyi amma kuma ba fa karko ta keyi ba. Kafin sauko
gida nayi magana da wani amini na akan nema maka yar wurinsa da aure kuma ya
bani damar hakan, sati mai zuwa rana ita yau, zamu tafi tare da kai a can kuga
juna a yi maganar ta zama daya. Tashi ka bani wuri wannan itace kalmar day a
rufewa Salim kofa da ita.
Ba
tare da bata lokaci ba kuwa Salima a cikin sanyin jiki da rashin tayi ya tashi
ya nufi kofa cike da damuwa.
SIN 28
LUBA CE DA SALMA DA NA’IMA A ZAUNE
Mamar
Na’ima za ta ce: Tabdi wai jiran
jira, Kare jiran tsakin mai toke, saboda Allah Salma yanzu ina zance hankali a
nan?. Wata kilama samarin nan tuni sunyi aurensu sun manta da ku. Domin bawata
yarjejeniyace a tsakaninku da su ba. Kawai daurare ku keyi na banza to ni bazan
zan yarda da hakan ba Salma. A cikin damuwa. Bayan ta gama sauraren abin da
yarta Salma ta gaya mata.
Salma:
A’a Umma kar kiyi haka, ki bari mubi lamarin a hankali da ya ke sai ranar
lahadi ne zan koma Abuja zanyi amfani da ranar Assabar a matsayin damar da
naked a ita mutafi tare da ita gidansu. Salima itama inaso inji ta bakinta yaso
daga nan zamu iya daurare ta hanyar da hotunan nan suka zo insha Allahu koma
meye gaskiyar lamarin zata bayyana.
Hajiya
Luba: Salma, karki daurewa yarinyar nan gindi a cikin sha’anin karya ta fada
tare da nuna Na’ima da ke zaune agefe dayan kujerar, wanda ya ke ita dai ba ta
ce uffan ba a duk cece kucen da mahaifiyar tad a yayar tata sukeyi.
Salma:
haba Umma ai bah aka bane kinsan da rashin kira Karen bebe ya bata.
Hajiya:
Bayan duk Shirun da ta yi ne tanisa tace tau ku kuka sani.
FADE
SIN 29
CAMERA NA BUDEWA
Hajiya
Aisha da yarta Salima ce yayin da Aisha ta ke zaune a kan kujera yarta Salima
ta dora kanta akan kafadar mahaifiyar tata sai hawayen bakin ciki ke famar
kwaranya a idanuwanta. Ya yin da mahaifin ta Alhaji Yusha’u yake a tsaye yana
ta famar safa da marwa agaban kujerar da suke zaune akan ta sai musiba yak eta
famaryi. Adalilin zuwan da Salima ta yi wurin Auwal domin yima sa kashedi ko
(Barazana).
Alhaji
Yusha’u: Yanzu nasan wana Haifa kuma da wana ke zaune a gida daya, tabbas
Salima tabbas kin nunamin cewa ke ci kakkiyar yar ta’addace kuma maras mutunci.
To, amma kafin kije kiyi masa barazanar kona shi dashi da mahaifan nasa meya
hana ki farad a mu din nan tukuna?. Ya zamana duniya ta baki lambar yabo
(award) kafin ki kona iyayen wasu naki kika fara konawa.
To,
bara in gaya miki in duk garin nan zai kama da wuta baza abi ra’ayin naki ba,
kuma tabbas kinyi nasara a wannan karon domin iyayensa sun nuna cewa in ke
kadaice Ya mace a duniya bazai aureki ba. Domin ba irinki suke nufi ba, uwa
marar tarbiyya, amma kuma ki sani har wayau ina yi miki albishir da rashin sa’a
domin har yanzu dai jiya iyan kinada sabon alkawarin wani akanki wanda bakisan
waye shi ba, balanta na inda zaki taraddashi kiyi masa rashin mutunci kuma
tabbas ranar tana cika za suzo kuma inda suka zo nan za a shafa fatihar aurenku
sai naga ta tsiyar lukin iya kamin indawo ki tabbatar kin babbaka gidan nan.
Kalmar da ya fada tare da buga hannun rigarsa ya sa kai ya tafi abinsa. Ita ce
kuwa kalmar da tasake sanya Salima tafashe da kuka mai kara har sai da ta
runtumo jikinta gaba daya akan cinyoyin mahaifiyarta ta bata ce dasu uffan ba a
duk jidalin nan da ake ta zubawa.
SIN 30
Salim
ne a zaune cikin wata gadinar fulawa mai ban sha’awa ya yin da Salima ta bullo
masa ta baya ba tare da ya sani ba tana tatta kowa a hankali a hankali har sai
da ta zo gab da shi ta bayansa sai ta karkada masa ganyen da ke rike a hannunta
a gefen kunnensa na hagu, ya sa hannu ya kakkabe batare da ya waigaba kafin
kace kabo tasake karkada masa abangaren dama, ya sake taba wurin kafin ajima
yaji abin abayan wuyansa. Da yaji tsalguwar ta soma yawa sai ya waiga don
tantance meyake faruwa namfa yaci karo da Salima ce ke da wta irin kwalliya
abin sai wanda ya gani tana ga nin ya waigo kuwa saita bushed a dariya ta juya
aguje tanufi inda tafito shikuwa Salim yace dawa aka hadani ba da ita ba, ya bi
ta da gudu danufin ya cimmata ya kamata haka dai sukayi ta bode – bode a cikin
fulawowin amma bai smau kamata ba.
SAI WAKAR DA SUKAYI TA WASALI DAYA
SALIM
SALIMA
SIN 31
Salim
ne a kwance dakinsa yana yan mirgine mirgine da yan juye – juyen kai alamar zai
fako daga baccin da ya keyi wanda a cikine ya yi mafarkin haduwarsa da Salima
bayan day a falko ne ya zabura ya tashi zaune a hargitse yana yan salatoci. A
cikin yanayin damuwa wanda said a takai ya yi tagumi idanuwansa suna kallon
sama yana nazari irin halin da ya sami kansa a ciki.
FADE
SIN 32
Na’im:
Hakika wannan shine abinda ya faru bayan rabuwarmu da ku amakaranta.
Salima:
kamar yadda kikaji Yaya Salim ya fada yanzun nan
Salima:
Ai Na’im da kai har yayanka naku wasa ne domin kuwa byaan mun rabu daku a
makaranta da shekarar daya ne a kayi auren anty Salma yayar Na’ima da Salmanu
abin yayi matukar burgemu kasancewar sunayensu sunzo iri daya wasali dayane
ban-banci, muma muka fitinu da matsa nancin gurin samarinmu suzamo haka. Wanda
nan take faruwar hakan tajefamana kakkarfan tarnaki a zukatanmu wanda ayau
tsawon shekaru biyu kenan muna fama da wannan kurji a zukatammu ta yaya zamu
samu irin nasarar da Auty Salma ta samu? Sai yau gashi kamar da ga sama mun
hade wuri daya da ku yayin da ukubar iyaye ta addabemu akan maganar aure.
Salim:
Eh, haka ne amma wani hanzari ba gudu ba Salima; Na’ima mun biyo adirehin da
kuka bamu ne kawai don karbar mantuwar mu dake hannun ku amma badon kulla wata
alakar soyayya ko aure ba. Domin kuwa mahaifina yayanke shawarar aurar min yar
amininsa, kuma na tabbatar ta haka zai yankewa dan uwana irin mummunan hukuncin
day a yanke min.
Wannan
itace kalmar da take fitowa daga bakin Salim yayin da yake mikewa a cikin
sanyin jiki. Daga zaunen da yake akan gaban motarda suka zo da ita. Na’im kuw
na jingina a jikin motar ne kusa da shi Salima tana gefen hagunsa Na’ima kuma
tana gefen damar Na’im. Itama jingine a jikin motar yayin da Salima ta kura masa
ido tayi tana kallonsa da irin furucin da ya ke fitowa bakinsa.
Na’ima:
tabbi jam, a she kuwa bacin yaba kafar baya kai kuwafa? Ina muka kwana? Ko
kaima duk maganar dayace? Na’ima ta kalli saurayinta Na’im a cikin damuwa
jejjefa masa tambayoyi amma sai kallonta kawai ya yi sanyaye a cikin mamaki
batare day ace da ita uffanba.
SIN 33
Sallamar
Na’im da izo kofa kusan duka daya ne, yayin da shigowarsa falon yayan mahaifin
nasa Dauda ked a wuya yaci karo dashi yana yiwa yayansa Salim gargadi shigowar
tasa ce kuwa tasa yayanke maganar da yake akanta yace yauwa! Na’im zonan yanzu
nake ce masa idan ya fita yakira min kai. Na’im kuwa a cikin girmamawa yazo a
gaban yayan mahaifin nasa ya rusuna zai zauna a kasa sai mahaifin yace dashi.
Alhaji
Dauda: A’a zauna kusa dad an uwan naka wato (Salim) da ke kan kujerar daya ta
gefen kafadar hagu da Alhaji Dauda bayan Na’im y agama gyara zamanne Alhaji
Dauda ya ci gaba da zance kamar haka:
Dauda:
Na’im da kai da Salim duk yaya nane ku, domin kuwa tun ranar da kanena wato
mahaifinku ya kwanta dama a dai – dai
shekararka ta uku a duniya na karbi tarbiyarka a hannuna ganin cea mahaifiyarka
bayan kasan nan bace. Bana so a ce kata shi ba a kusa da mu ba, yasa muka
hanata tafiya da kai. A kasarta ta haihuwa wato (maleshiya).
Daga
wannan lokacin zuwa yau ina zaton na sauke wasu daga cikin farillanku na
wajabci a kaina kamar ci da sha, sutura, ilmantarwa, lafiyarku da kuma
tarbiyya. A yanzu mataki na gaba shi ne maganar raya sunnar ma’aiki wato aure,
daya ke Salim ya gayamin cea akwai wadda kukayi alkawari aure da ita na keso
inji abakinka ko gaskiya domin inason a hada bikin naku lokaci daya ne.
Na’im:
a cikin yanayin jin nauyi ya rutsa yace gaskiya ne abba. Aishima yaya Salim
yana da wadda sukayi alkawali daya ke tayi.
Dauda:
Dakata Na’im baruwana dawannan zancen nariga nayi alkawari bazancen kwancewa
Salim yar aminina zan aura masa. Kalmar kuwa da tasa Salim da Na’im suka kalli
juna a lokaci daya a cikin yanayin damuwa.
SIN 34
Salima
da Na’ima ce a zaune a cikin dakin Na’ima na bacci a gidansu yayinda Na’ima
take zaune a bakin gado, ita kuma Salma ta na a tsaye ne daf da kafadarta tana
bata magana dangane da Halin tunanin da taga kanwar tata Na’ima tashiga.
Salma:
Na’ima aurefa nufin Allah ne kuma da ce da miji kowane irin daga gareshi ne,
don hakabana son ganinki a cikin irin wannan halin yakamata kalma da furucinta
yazo dai-dai da ringin din da wayar Na’ima tayi wannan ya zama sanadin dakatar
da zancenda Salma takoroyiwa Na’ima domin tuni hankalin Na’imar ya juya izuwa
ganin wane irin sako ne tasamu a wayarta ta, nan take kuwa Amadadin yanayin
fushin da take ciki sig a wani dan saurayin murmushi yak e to fuskarta ta ganin
cea sakon daga Na’im ne bada bata lokaci ba kuwa ta soma karanta sakon kamar
haka: Assalamu alaikum, Masoyiyar rayuwa tan a tabba ta tsawon kwanaki hudu da
muka rabu da juna kina a cikin irin halin da nasami kaina a ciki na damuwa,
amma yau ina mai yi miki albishir da cewa Abba ya bani damar zabin mata dakaina
wanda tuni kin sani na sani kece zabi na. amma sai dai kash Yaya Salim ya kasa
samun irin wannan damar, domin kuwa Abba ya nace akan bakarsa tacewa sai yar
amininsa da sukayi alkawari dashi.
Daya
ke karatu ne da takeyi a bayyane Salma ta riga taji komai Na’ima na kai suratun
wasika ne tace da ita To, kinga ga maganar wan an tafara fitowa dadin hakurin
kenan. Yanzu sai dai mutaru mutaya Salima ad addua’ar dacewa itama. Alokacin
nan kuwa da Salma ke wannan zancen fuskar Na’ima cike take da annuri ganin cewa
burinta zai cika bayan da hartana ganin kamar ya kubuce mata.
SIN 35
Salima da Na’ima
da Na’im da Salim ne suka jero akan hanya suna tafiya suna hira harma da dare-dare.
Kwatsam, sai su kaji kamar daga sama anhada birki a gabansu, yayinda suka ankara
wata motace ta alfarma ta bayyana agabansu, amma tuni Salima da Na’ima sun gane
ko wane ne sai dai Salim da Na’im sai mamaki kawai su ke yi tare da daukar abin
amatsayin rainin wayo na musamman. Kai abinfa kamar wasa karamar magana ta zama
babba domin tsaya war motar ke da wuya sai Alh. Yusha’u Baban Salima da ya ke
shi ne jaye da motar yayi wuf ya bude ganbun motan ya futo da hanzari yana cewa
ke
Alhaji Yusha’u: Salima ba na hanaki sauraron ko wane
saurayi ba in dai ba wanda na tsayar maki ba?. Salima da Na’ima tuni sun sha
jinin jikinsu tun kafin faruwar hakan sai faman kyarma su ke yi da kuma alamar I’inniyar
magana, amma basa iya furta komai saboda rashin hujja. Nan take shima Alhaji
Dauda ya bude gambun motarsa ya fito cike da mamaki
Alhai Dauda: Salim, Na’im! me zan gani haka? Su waye
wadan nan? Hauka ku ke yi ne?.
Alhaji Yusha’u: Amm! Alhaji Dauda dama ka kansu ne?
Alhaji Dauda: “Ai yaya na ne, wannan shi ne salim
din da nake nemawa yar wurinka.
Alhaji Yusha’u: Ikon Allah ai wannan itace Salima ‘Ya
ta da na yiwa Danka alkawarinta.
Alhaji Dauda: Allah Sarki!, tuwo na maina kenan. To,
dama kunsan juna ne? ya kalle ya tambaya
Na’im ne ka dai
ya samu damar magana.
Na’im: Abba dama ai wannan itace Salima wacce Yaya Salim ya ke so
tun da dewa amma gudun ya keta umurnin ka ne ya sa ya ki ya gayamaka.
Duk zancen nan
da ake kuwa, Salim da su Na’ima kawunan su a sunkuye ne alamar jin kunya.
Alhaji Yusha’u: To, kai kuwa fa, Na’ima ko? Shawaraki.
Ya fada a cikin yanayin dariya cike da farin ciki.
Na’im shi ma ya
soke kansa a kasa, ya shiga layin yan uwansa
SIN 36
Salma ce da Salima
da Na’ima da Mahaifiyarsu Na’ima Hajiya Luba a cikin gidansu suna al’jabin
wannan babban al’amarin da ya faru
Salma: To, kunga abin da nake gaya muku yau ga magana ta ta fito dama
ance mai hakuri ya kan dafa dutse harma ya sha romunsa.
Hajiya Luba: To, Fadi dai ke, wayan nan yaran,
wayan nan yaran, nacin su ba kadan bane. Da wannan gurin nasu bai cika ba da
ba’asan ya za a kwashe da su ba. Ta fada tare da nuna yar da Na’ima da yatsa.
Na’ima: Wallahi Umma ji muke kamar an saka mu----
Salima: A aljanna ko kawata?
Salima ta idar
mata da zancen da ta fara har ma suka tafa hannaye da juna a cikin yanayin farin
ciki.
Hajiya Luba: Kaicu!, kinga marasa kunya ko?
Salima: Ayyah! Umma ai ba rashin kunya bane farin ciki ne suke
bayyanawa, irin na masoyan zamani.
0 Comments
Post a Comment