DU’AUL MUSTAJABA - FALALAR AMBATON ALLAH MADAUKAKI DARASI NA 1
Allah tsarkakakken sarki kuma MadaukakiYa ce: “Ku tuna da Ni, Ni
kuma zan tuna da ku, kuma ku yi godiya zuwa gare Ni, kuma kada ku butulce min”.
Don haka wannan ya nuna cewa duk wanda ya kasance yana tuna Allah a
koda yaushe Allah zai tuna dashi zai taimaka masa, zai kuma kasance gatansa a
duk inda ya sami kansa.
Kuma Allah Madaukaki Y ace: “Ya ku wadanda suka yi imani! ku ambaci
Allah, amboto mai yawa. Kuma ku tsarkake Shi, a safiya da marece. Shi ne wanda
ke tsarkake ku, da Mala’ikunsa kuma suna yi muku addua, domin Ya fitar da ku
daga duhu zuwa haske. Kuma Ya kasance Mai jin kai ga muminai. Gaisuwarsu a ranar
da suke haduwa da Shi ita ce “Aminci”, kuma Ya yi musu tattalin wani sakamako
na karimci”.
Babu shakka Allah Ya yi kira ga wadanda suka yi imani da su tsarkake
Allah ta hanyar ambatonsa cikin safiya da marece, tare da tabbacin zuwa garesu
da cewar idan suka yi hakan shima Allah zai tsarkake su tare da mala’ikunsa da
basa saba masa, zai kuma yi masu jagora ta hanyar dorasu a bisa hanya ma
daidaiciya ya kuma kawar masu da duhun kafirci da zalunci. Kuma ya kasance mai
tausayawa zuwa ga muminai. Bayan haduwar su a cikin rahamarSa zasu kasance suna
yiwa juna barka da cewa “Salam/Aminci, Aminci” zasu kuma dauwama a cikin
karimcin ubangijinsu.
Kuma Allah Madaukaki Ya ce: “Ka hakurtar da ranka tare da wadanda
ke kiran ubangijinsu, safe da maraice, suna nufin yardarSa. Kuma kada idanunka
su juya daga barinsu, kana nufin kawar rayuwar duniya. Kuma kada ka bi wanda
Muka shagaltar da zuciyarsa daga ambatonMu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhali
kuwa al’amarinsa ya kasance yin barna”.
Allah ta’ala ya na bawa manzonsa hakuri tare da wadanda sukayi
imani masu yawan ambaton Allah a cikin safiya da yamma, masu nufi da neman yardar
Allah. Tare da fadakar musu cewa kada su juya zuwa ga barin nagartattun bayi
idanuwansu su koma ga kawar duniya ko kwadayin duniyar wasu wadanda suka
kasance masu yin barna.
Kuma Allah Madaukaki Ya ce: “Kuma wanda ya bijire daga ambotoNa,
to, hakika Rayuwa mai kunci ta tabbata a gareshi, kuma muna tayar das hi a
ranar kiyama yan makaho”.
Allah Madaukakin Sarki Ya ce: “Kuma wanda ya makanta daga barin
amboton Ubangiji mai rahama, to, za mu sabauta shaidan a gareshi, watau shi ne
abokin sa.
Wadanda basa ambaton Allah zasu kasance cikin kunci da tashin hankali
a ranar kiyama haka kuma anan cikin duniya shaidan ne zai zama aboki garesu.
Kuma Manzon Allah ya ce: “Allah madaukaki yan cewa: “Ni ina inda
bawana ya zace ni. Kuma ina tare dashi idan ya ambace Ni, idan ya ambace Ni a
cikin ransa sai in ambace shi a zatina. kuma idan ya ambace Ni a cikin taro, to, zan ambace shi a cikin
taro mafi alhairi daga nasa. kuma idan ya kusanto gare ni da taki day azan kusanto
gashi da zira’I guda; kuma idan ya kusanto zuwa gare ni da zira’I guda zan
kusanto zuwa gare shi da gaba gudu; kuma idan ya zo mini yan mai tafiya, to,
zan zo masa ina mai gaggawa”. Ahmad, Bukhari, Muslim, Tirmizi, Nisa’I da Ibnu
Majah suka ruwaito shi (Hadisin Abu Huraira R.A).
Kuma Annabi ya ce: “Mutane
ba zasu zauna suna ambaton Allah madaukaki ba face mala’iku sun kewaye su, kuma
rahama ta lullube su, kuma natsuwa ta sauka a garesu, kuma Allah madaukaki ya
ambace su a wajen wadanda suke wajensa”. Ahmad, da Muslim suka ruwaito (Hadisin
Abu Huraira R.A)
Kuman Manzon Allah Yace : “Lalle, Allah zai tashi wasu mutane ranar
alkiyama alhali a cikin fuskarsu akwai haske, suna zauna a kan mimbarai na lu’ulu’u,
mutane suna kwadayin halin da suke ciki, gasu kuwa ba annabawa ba ne ko
shahidai”. Sai wani balarebe ya durkusa a kan gwiwoyinsa sai ya ce : Ya manzon
Allah! siffanta mana su, don mu sansu”. Sai ya ce : “Su ne masu soyayya don
Allah daga kabilu daban-daban da garuruwa daban-daban da suke taruwa a bisa
ambatun Allah. Dabarani ne ya ruwaito kuma hadisi ne mai kyau daga (Abud-Darda’I
R.A)
Kuma Annabi Ya ce: “Mafificin zikiri shine ‘La’ilaha Illallah’,
kuma mafificiyar addu’a it ace Alhamdulillah”. Tirmizi, Nisa’I, Ibnu Maja, Ibnu
Hibban da Hakim suka ruwaito shi (Hadisin Jabir R.A)
Annabi (S.A.W) ya ce: “Mutum da dai bai fadi ‘La’ilaha illallah ba
yana mai tsarkake niyyarsa face an bude masa kokofin sama har sai an sadar da
ita zuwa al’arshin Allah, muddin ya nisanci manyan zunubai”. Tirmizi ya ruwaito
shi (Hadisin Abu Huraira R.A)
Kuma Annabi (S.A.W) ya ce: “Kewa yayin mutuwa a cikin kabari ko a
lokacin tashi daga kabari ba za ta kasance bag a ma’abuta ‘Laila ha’illah’.
Kamar cewa ni ina duba zuwa gare su yayin tsawar tashin kiyama suna karkade
kawunansu, suna cewa :Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya tafiyar mana dab akin
ciki’ Dabarani ya ruwaito (Hadisin Dan Umar R.A)
Annabi (S.A.W) ya ce :Yan aljanna ba za su ga hasara a kan wani abu
ba, face a kan wani lokaci da ya wuce su lokacin da suke a duniya ba tare da
sun ambaci Allah mabuwayi mai girma a cikinsa ba.” Dabarani dai Baihaki suka
ruwaito (Hadisin Mu’azu R.A)
Annabin Allah (S.A.W) ya ce :Babu wani mutum da zai fadi La’ilaha
illallah sau dari (100 times) face Allah madaukaki ya tashi shi ranar kiyama
fuskarsa tana haske kamar wata daren sha biyar. kuma a wannan ranar ba za a daukaka
aikin wani ba mafi falala daga aikinsa face wanda ya fadi misalign fadinsa ko
ya kara akai”. Dabarani ya ruwaito shi (Hadisin Abud Darda’I R.A)
Kuma
Annabi (S.A.W) yana cewa “La’ilaha illallah Wahdahu Lasharikalah Lahul Mulku
walahul hamdu Wa huwa ala kulli shai’in kadari” 10x Ma’ana (Babu abin bautawa
da gaskiya fa ce Allah, madaukaki, baida abokin tarayya a tare dashi, Mulki na
sa ne, kuma godiya ta tabbata a gareshi kuma shi mai iko ne abisa kowane abu.
Sau Goma. Ya kasance yana da kwatankwacin ladar yanta bayi hudu daga yayan
Annabi Isma’il (A.S)”. Buhari da Muslim da Tirmizi da Nisa’I suka ruwaito shi
(Hadisin Abu Ayyub (R.A)
ALSO REAL ADDU’A DAGA LITTAFIN DU’AUL MUSTAJABA - GABATARWA
0 Comments
Post a Comment